Manyan Labarai A Yau
Wani jirgin ruwa da ya dauko fasinjoji 90, mata da yara ya kife a yankin karamar hukumar Borgu ta jihar Neja, an tabbatar da mutuwar mutane 29 daga ciki.
Kungiyar dattawan Arewa ta mika bukatunta ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinuvu kan matsalar rashin tsaro. Ta nuna cewa akwai bukatar a ayyana dokar ta baci.
An tabbatar da rasuwar tsohon dan takarar gwamnan jihar Ondo karkashin inuwar jam'iyyar SDP, Otunba Bamidele Akingboye a gidansa da ke jihar Legas.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya karbi bakuncin 'yan kungiyar Buhari a fadarsa da ke Abuja. Ya gaya musu cewa ba zai iya nada kowa a kan mukami ba.
Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam'iyyar LP a 2023, Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya taso Nasir El-Rufai a gaba kan zargin da ya yi wa gwamnatin Bola Tinubu.
Wata Kotun Majistare a jihar Ebonyi ta bayar da umarnin a tsare wani malamin addini bisa zargin yunkurin kisan kai, haddasa gobara, da sauran laifuffuka.
Jigo a jam'iyyar APC a jihar Kano, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya caccaki tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, bayan ya yi kalaman zargi kan gwamnatin Bola Tinubu.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun yi awon gaba da wani basarake a jihar Kogi. 'Yan bindiga sun sace basaraken ne lokacin da yake kan hanyar dawowa daga taro.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin a sake duba ayyukan samae da tsaro a jihar Katsina. Ya umarci a kara sayo kayan aiki ga jami'an tsaro.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari