Manyan Labarai A Yau
NiMet ta gargadi ‘yan Najeriya kan yiwuwar saukar ruwan sama da iska mai karfi a jihohi da dama, ta ba da shawarwari don kariya daga haɗurra da ambaliya.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Ezenwo Wike, ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmed kan janye dokar ta bacin da ya sanya a jihar Rivers.
Wani jagoran 'yan bindiga, Isiya Akwashi Garwa, ya sako mutanen da ya sace a jihar Katsina. Jagoran 'yan bindigan ya sako mutanen ne saboda yarjejeniyar sulhu.
Ministan kudi, Wale Edun ya bayyana cewa gwamnatin tarayya za ta maida shirin tallafin ragw radadi ya zama a na kowace shekara, ya ce mutane da dama sun amfana.
Hadimin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, Daniel Bwala, ya yi martani mai zafi ga Alhaji Atiku Abubakar kan ikirarin cewa ana fama da yunwa a Najeriya.
Shugaban rukunin kamfanonin Dangote Group, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana cewa direbobin sa ke aiki a karkashinsa na samun nunkin mafi karancin albashi hudu.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya janye dokar ta bacin da ya sanya a jihar Rivers. Shugaba Tinubu ya bayyana cewa zaman lafiya ya dawo a jihar mai arzikin mai.
Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya fito ya yi magana kan rahotannin da ke cewa zai sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa ADC. Ya yi watsi da batun.
Jamhuriyar musulunci ta Iran ta zartar da hukuncin kisa ta hanyar rataya kan mutumin da ya rika tura wa Isra'ila bayanan sirri, ta ce babu wanda za ta daga wa kafa.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari