Manyan Labarai A Yau
Matatar Dangote ta yi tayin biyan albashi ga ma'aikatan da ta kora saboda zargin cin amana. Sai dai kungiyar PENGASSAN ta ki amimcewa da bukatar matatar.
Tsohon shugaban kasan Najeriya, Olusegun Obasanjo, ya yi magana kan rikicin Boko Haram. Ya bayyana cewa ya kamata a dauki kwararan matakai don magance matsalar.
Kotu ta yanke wa shahararren mawakin hip-hop, Sean “Diddy” Combs, hukuncin zaman gidan yari na fiye da shekaru huɗu kan tuhumar da ta shafi karuwanci a Amurka.
An shiga tashin hankali a karamar hukumar Ose da ke jihar Ondo yayin da wasu matasa suka lakadawa sarki da dansa dukan tsiya, suka nemi yiwa matar sarki tsirara.
Shugaba Bola Tinubu ya ce soke bikin cikar Najeriya shekara 65 da samun 'yancin kai ya ba shi hutu sosai, yayin da ya kaddamar da cibiyar Wole Soyinka a Legas.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi shekara biyu a kan mulkin Najeriya. Ana ganin wasu 'yan Arewa na iya mara masa baya don yin tazarce a zaben shekarar 2027.
Rahotanni daga jihar Ogun sun bayyana cewa wata tanka da ta dauko man fetur ta fashe a kan totin Abeokuta zuwa Sagamu, ana fargabar mutane da dama sun mutu.
Jam’iyyar ADC ta shiga jimami bayan mutuwar mataimakin sakataren hulda da jama'a na Imo, Hon. Ugochimereze Asuzu, wanda aka bayyana a matsayin babban jigon Inyamurai
Yara hudu sun jikkata da wata kwalbar barkonom tsohuwa mai sanya hawaye ta fashe a Sharada da ke cikin birnin Kano, yan sanda sun gudanar da bincike kan lamarin.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari