Manyan Labarai A Yau
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta ragargaji shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu. Ta nuna cewa shugaban kasan yana yi wa rashin tsaro rikon sakainar kashi.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai harin ta'addanci a jihar Neja. 'Yan bindigan sun hallaka wani shugaban 'yan sa-kai tare da yin garkuwa da wasu mutane.
Gwamnatin jihar Kano ta bakin majalisar Shura ga gargadi malaman addini kan yin magana dangane da binciken da ake yi kan Sheikh Lawan Shu'aibu Abubakar.
Tsohon dan takarar gwamnan jihar Legas, Abdul-Azeez Adeniran, ya gargadi tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, kan yin takara da Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi ta'aziyya kan rasuwar tsohon Jakadan Najeriya a kasar Tunisia. Marigayin ya rasu yana da shekara 82 a duniya.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai hari a babban birnin tarayya Abuja. 'Yan bindigan sun kashe wani babban likita tare da yin garkuwa da 'ya'yansa.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yi kira da babbar murya ga mutanen da ke rayuwa a kan iyaka. Ya bukaci ka da su bari 'yan ta'adda su kore su.
Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya ayyana Litinin a matsayin hutu don girmama malamai, yayin da UNESCO ta ce duniya na bukatar karin malamai miliyan 44 kafin 2030.
Sarkin Kirawa ya tsere zuwa Kamaru bayan Boko Haram sun kai hari suka ƙone fadarsa, suka kashe mutane biyu, yayin da dubban jama’a suka gudu daga Gwoza.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari