Manyan Labarai A Yau
Dakarun sojojin Najeriya masu aikin samar da tsaro sun samu nasara kan 'yan bindiga a jihar Sokoto. Sojojin sun kashe tsageru masu yawa yayin artabun da aka yi.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi afuwa ga wasu 'yan Najeriya. Shugaban kasan ya yi afuwar ne bayan samun shawarwari daga wajen wani kwamiti.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta aika sakon jan kunne ga sabon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Joash Amupitan. Ta bukaci ya yi adalci.
Premium Times ta ce za ta gurfanar da kakakin tsohon minista Robert Ngwu a kotu kan zargin karɓar cin hancin N100m, yayin da Nnaji ya yi murabus daga mukaminsa.
Jami'an tsaro na hukumar shige da fice ta kasa (NIS), sun samu nasarar cafke wani matashi kan zargin sato motar asibiti daga Jamhuriyar Nijar makwabtaka.
Majalisar Koli ta Kasa ta amince da nadin Farfesa Amupitan daga jihar Kogi a Arewa ta Tsakiya a matsayin wanda zai gaji Mahmood Yakubu a hukumar zabe INEC.
Tsohon gwamna kuma Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu ya karyata ikirarin Olusegun Obasanjo cewa labarin da ake yadawa cewa ya nemi zango na uku ba gaskiya ba ne.
Majalisar dattawa ta rantsar da sababbin sanatoci biyu, ta karɓi wasikun Shugaban Tinubu kan nadin shugabannin hukumomi, yayin da Sanata Kelvin Chukwu ya koma APC.
Tsohon gwamnan jihar Abia, Sanata Orji Uzor Kalu, ya yi magana kan tasirin Peter Obi a yankin Kudu maso Gabas. Ya ce ya fi shi zama dan siyasa mai muhimmanci.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari