Manyan Labarai A Yau
Gwamnatin Kamaru ta sanar da cewa za ta gurfanar da matasa akalla 20 da aka kama a kotun soja kan zanga zangar bayan zaben shugaban kasa saboda tayar da tarzoma.
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ya karyata zargin kisan Kiristoci a Najeriya. Ya bayyana cewa ko kadan babu kamshin gaskiya.
Gwamna Bala Mohammed ya kafa sababbin masarautu 13 da hedkwatocinsu a Bauchi, ya kuma soke tsohuwar masarautar Sayawa tare da kafa masarautar Zaar.
Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa Watau FRSC reshen jihar Neja ta tabbatar da fashewar tankar mai a titin Bida da yammacin yau Talata, ana fargabar rasa rayuka.
Kotun Koli ta shirya yanke hukunci kan karar da ke kalubalantar dokar ta bacin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya a jihar Rivers har ta wata shida.
Tsohon shugaban Faransa Nicolas Sarkozy ya shiga gidan yari bayan an kama shi da laifin karbar kudin kamfen daga Gaddafi, amma ya ce gaskiya za ta bayyana.
Gwamna Alex Otti na jihar Abia ya musanta labarin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa ya fice daga jam'iyyar LP zuwa APC mai mulkin kasar nan.
Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta sake gamuwa da koma baya bayan dan majalisar wakilai daga jihar Benue, ya tattara kayansa ya koma jam'iyyar APC.
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bayyana cewa gwamnonin jam'iyyun adawa na yin tururuwa zuwa jam'iyyar APC ne saboda manufofin gwamnatin Tinubu.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari