Manyan Labarai A Yau
Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Obot Akpabio, ya yi tsokaci kan dalilin da ya sa mata ba sa iya samun kujerun siyasa sosai a kasar nan.
Tsohon karamin ministan man fetur, Timipre Sylva ya karyata rahoton da ake yadawa cewa yana da hannu a zargin shirin kifar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya sassauta hukuncin kisan da aka yanke waMaryam Sanda, ya dawo da shi hukuncin daurin shekaru 12 a gidan gyaran hali.
Majalisar dattawa ta kammala aikin tantance sababbin hafsoshin tsaron da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada. Ta amince da nadin da aka yi musu.
Sabon hafsan sojojin kasan Najeriya, Manjo Janar Waidi Shaibu, ya sha alwashin ragargazar 'yan ta'addan Lakurawa da ke kai hare-hare a yankin Arewaci.
Jam'iyyar PDP mai mulki a jihar Zamfara ta rasa daya daga cikin 'yan majalisun da take da su. Dan majalisar ya sauya sheka zuwa jam'iyyar APC mai adawa.
Gwamnatin jihar Kebbi ta fito ta yi magana kan rahotannin da ke cewa akwai wani boyayyen filin jirgin sama a Argungu. Ta bayyana cewa karya ce tsagwaronta.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta bayyana shugabancin da ta amince da shi a jihar Adamawa. ADC ta dauki matakin ne bayan jam'iyyar ta rabu gida uku.
Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaru Bago ya ayyana ranakun Alhamis da Juma'a, 30 da 31 ga watan Oktoba, 2025 a matsayin hutu saboda zaben kananan hukumomi.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari