Manyan Labarai A Yau
'Yan ta'adda dauke da makamai sun sake kai harin ta'addanci a jihar Neja. Tsagerun sun kona ofishin 'yan sanda tare da kayan amfanin gona na manoma.
Gwamnatin Tarayya ta yi wa Super Eagles alkawarin $10,000 kan kowace kwallo da za su ci a wasan da za su fafata da 'yan wasan Mozambique a AFCON 2025.
Wata babbar kotun tarayya da ke birnin Abuja ta yi hukunci kan bukatar kwamishinan kudi na jihar Bauchi ya shigar a gabanta. Ta ki yarda ta ba da belinsa.
Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta yi babban rashi a jihar Sokoto bayan ficewar wani babban jigo a cikinta. Sanata Abdallah Wali ya raba gari da PDP.
Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United da ke kasar Ingila ta raba gari da mai horar da manyan 'yan wasanta, Ruben Amorim bayan ya yi kunnen doki da Leeds.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC), ta yi magana kan shari'ar tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello. Ta ce lamarin yana gaban kotu.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ci gaba da shirye-shiryen komawa jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya. An ji mutanen da za su bi shi daga NNPP.
An binne tsohon Kwamishinan Ilimi na jihar Kaduna, Alhaji Suleiman Lawal Kauru, a Zaria bayan ya rasu yana da shekaru 78 a asibitin koyarwa na ABUTH da ke Shika.
Yara 11 sun tsinci harsasan kakkabo jiragen sama a magudanar ruwa a Maiduguri; sojoji sun killace yankin yayin da aka bai wa yaran kyautar kuɗi saboda jarumta.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari