Manyan Labarai A Yau
Sanata Mai wakiltar Kogu ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta fafatawa da jami'an hukumar NIS lokacin da aka kwace mata fasfo a filin jirgin sama a Abuja yau Talata.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da karin girma ga Manjo Janar Abdulsalam Bagudu Ibrahim, wanda ya taba zama mukaddashin hafsan sojojin kasa.
Jam'iyyun adawa sun nuna rashin amincewarsu da zaben kananan hukumomin da aka gudanar a jihar Neja. Sun yi zargin cewa an tafka gagarumin magudin zabe.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya yi magana kan barazanar da shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya yi ta kawo farmaki a Najeriya.
Tsohon dan takarar shugaban kasa na LP, Peter Obi ya bukaci Najeriya da Amurka su zauna su tattauna domin hada kai wajen kawo karshen ta'addanci a kasar nan.
Hadimin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, Daniel Bwala, ya bayyana cewa dole ne Amurka ta nemi iznin Najeriya kafin daukar matakin sojoji a kasar nan.
Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya mika sakon ta'aziyya da addu'o'in neman rahama bisa rasuwar Durbin Kano, Muhammad Lawan Koguna, ya ce an yi rashi.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu gagarumar nasara kan 'yan bindiga yayin wani artabun da suka yi a jihar Kano. Sojojin sun kuma kwata kayayyaki.
Tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya yi martani mai kaushi kan shugaban kasar Amurka, Donald Trump, saboda barazanarsa ga Najeriya.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari