Manyan Labarai A Yau
Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya yi karin haske kan dalilinsa na shigar da jam'iyyar PDP kara a gaban kotu. Ya ce yana son kwatar hakkinsa ne.
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf na shirin gabatar da kasafin kudin 2026, wanda zai kafa tarihin zama na farko da zai lakume akalla Naira tiriliyan 1 a jihohin Arewa.
Tsohon kwamishinan yada labarai, Don Adinuba ya ce labarin da ke yawo cewa tsohon gwamnan jihar Anambra, Willie Obiano ya mutu a birnin Landan na Birtaniya.
Yan majalisa 12 a Ondo sun fara shirin tsige kakakin majalisar jihar, Olamide Oladiji bisa zargin rashawa, karkatar da N50m da sabawa kundin tsarin mulki.
'Yan majalisar wakilai na jam'iyyar NNPP sun fito sun yi bayani kan jita-jitar da ke cewa suna shirin sauya sheka daga jam'iyyar zuwa wasu jam'iyyu.
An samu hatsaniya tsakanin dakarun sojojin Najeriya da jami'an 'yan sanda a jihar Benue. Fadan wanda ya auku sakamakon sabani ya jawo an jikkata mutum daya.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta ragargaji shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan bashin da gwamnatinsa za ta kara ciyowa. Ta ce hakan bai dace ba.
Wani jirgin kasa da ke dauke da fasinjoji a hanyar Kaduna zuwa Abuja ya sake samun matsala. Jirgin kasan ya samu matsala ne bayan ya tashi daga Kaduna.
'Yan ta'addan kungiyar Lakurawa sun kai harin ta'addanci a jihar Sokoto. 'Yan ta'addan sun hallaka bayin Allah ciki har da wata mata mai dauke da juna biyu.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari