Maiduguri
Gwamnatin tarayya, ta bakin hukumar raya shiyyar Arewa maso Gabas ta bayyana cewa rashin kargon gini da cushewar ruwa a madatsar Alau ya jawo ambaliya a Maiduguri.
Gwamnatin Najeriya ta kashe N26m domin aikin gyaran madatsar Alau a ranar 29 ga watan Yulin 2024, kusan wata daya kafin ambaliyar ruwa ta mamaye Maiduguri.
Hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) ta ce zuwa yanzun ta gano gawarwakin mutum 30 waɗanda suka rusu a ambaliyar ruwan da ta kusa shafe Maiduguri.
An wayi gari a Maiduguri bayan an kwana da ambaliyar ruwa, mutane sun fara komawa gida yayin da harkoki suka fara dawowa. Wasu sun kwana a bakin hanya.
Ambaliyar ruwan shekarar 2024 a Maiduguri ta jawo mutane sama da 200,000 sun rasa gidaje. Haka zalika an nemi yara kanana an rasa yayin da ambaliyar ta yi tsanani.
A safiyar Talata ne jama'ar Maiduguri a jihar Borno su ka wayi gari da ambaliya mafi muni a shekaru 30, inda ta lalata muhimman wurare, har da makabartu.
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bada tabbacin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta magance kalubalen ambaliyar ruwa a Najeriya.
Shugaba Bola Tinubu ya umarci hukumar NEMA ta gaggauta kai dauki ga wadanda ambaliyar ruwa ta rutsa da su a Maiduduri, yana mai jajantawa gwamnatin Borno.
Ambaliyar ruwa ta rusa gidan dabbobi da ke Maiduguri a jihar Borno. Dabbobi kamar kada da macizai sun shiga gari ta cikin ruwa. Kashi 80 na dabbobi sun mutu.
Maiduguri
Samu kari