Kananan hukumomin Najeriya
Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia ya rantsar da shugabannin kananan hukumomi 23 na jihar. Gwamna Hyacinth Alia ya ba su shawarwari kan harkokin mullki.
Rahotanni sun ce 'yan bindiga sun fatattaki ciyaman a lokacin da suka kai farmaki sakatariyar karamar hukumar Ikwere da ke jihar Ribas a ranar Litinin.
Ana zargin cewa wasu bata gari sun cinnawa sakatariyar karamar hukumar Eleme wuta awanni bayan rantsar da sababbin ciyamomin kananan hukumomin Ribas.
Shugaban kungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan Bauchi, Bala Mohammed ya yabi yadda gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara ya yi tsayin daka wajen zaben kananan hukumomi.
Hukumar zaben jihar Akwa Ibom, AKISIEC ta sanar da sakamakon zaben kananan hukumomi da aka gudanar inda PDP ta lashe kujeru guda 30 daga cikin 31.
Hukumar zaben jihar Rivers, RSIEC ta sanar da nasarar dan takarar jam'iyyar AA, Adolphus Enebeli a yau Lahadi 6 ga watan Oktoban 2024 bayan zaɓen kananan hukumomi.
Gwamna Sim Fubara na jihar Ribas, a yau (Lahadi) zai rantsar da sababbin zababbun shugabannin kananan hukumomin jihar. An ce za a yi rantsarwar da karfe 4.
Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Benue ta lashe zaben kananan hukumomin da aka gudanar a jihar. APC ta lashe dukkanin kujerun ciyamomi da kansiloli.
Fitaccen dan gwagwarmaya a yankin Neja Delta, Asari Dokubo ya gargadi rundunar sojoji da yan sanda a jihar Rivers bayan ganin jirgi na shawagi a saman gidansa.
Kananan hukumomin Najeriya
Samu kari