Labaran Duniya
Mutane sama da 300,000 sun bar gidajensu bayan harin bama-baman da Isra'ila ta ƙara kaiwa birnin Tehran yayin da Iran ta nuna alamun amincewa da batun sulhu.
Isra'ila ta kashe sabon babban hafsan sojojin Iran, Ali Shadmani, a harin da ta kai Tehran. An ji fashe-fashe biyu a Tabriz, yayin da rikicin ya shiga kwana na 5.
Yan Majalisar dokokin kasar Iran sun kaɗa kuri'ar amincewa da Ali Madanizadeh a matsayin sabon ministan tattalin arziki da kudi don shawo kan matsalolinta.
Isra'ila ta farmaki gidan talabijin mallakin gwamnatin Iran a Tehran yayin watsa shirye-shirye. Iran ta yi Allah wadai da tare da yin kira ga MDD ta dauki mataki.
Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan Isra'ila, wanda ya kashe mutane takwas. Isra'ila ta gargadi mazauna Tehran da su fice daga garin, ta karya lagon Iran.
Cibiyar CPPE ta bayyana cewa za ta samu tagomashi ta fannin fitar da ɗanyen mai sakamakon yakin Isra'ila da Iran, amma ta ce akwai matslolin da za su biyo baya.
Firaministan kasar Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya bukaci mazauna birnin Tehran na kasar Iran da gaggauta ficewa yayin da ake ci gaba da kai hare-hare.
An kama wani mutum mai suna Esmail Fekri da laifin yi wa kasar Isra'ila leken asiri a kasar Iran. Kotun Iran ta rataye shi bayan tabbatar da aikata laifin.
Ministan harkokin waje na kasar Jamus, ya bayyana cewa kasashen Faransa, Birtaniya da Jamus sun shirya zama kan teburij tattaunawa da kasar Iran.
Labaran Duniya
Samu kari