Labaran Duniya
Isra'ila ta tabbatar da kashe kwamandan Hamas Hakham Muhammad Issa Al-Issa a Gaza, inda take zargin shi da tsara harin 7 ga Oktoba da gina sojojin Hamas.
An gano wani jirgin sama da ya yi hatsari a Alabama ba tare da matuƙi ko fasinjoji ba, lamarin da ya zama abin mamaki da ya sa hukumomi suka fara bincike sosai.
Yayin da aka kwashe kwana 12 ana gwabza fada, shugaban Amurka Donald Trump ya fadi yadda ya kare rayuwar jagoran addini, Ayatollah Ali Khamenei na Iran.
Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu na tsaka mai wuya da wata kotu ta ki yarda ta ɗage zaman sauraron shari'ar da ake tuhumarsa da karɓar na goro.
Wadanda suka tsira daga yaƙin duniya na II da wasu shugabanni a Japan sun nuna damuwa da kalaman da shugaban Amurka, Donald Trump ya yi kan harin Iran.
Iran ta kashe mutum shida, ta kama daruruwa bisa zargin suna yi wa Isra'ila leƙen asiri, lamarin da ya jawo martani daga ƙungiyoyin kare hakƙin bil'adama.
Yakin da aka kwashe kwana 12 ana yi tsakanin Iran da Isra'ila ya samo asali ne kan zargin shirin mallakar nukiliya wanda ake daukarsa a matsayin makami mai haɗari.
Alamu na nuna cewa jamhuriyar Musulunci ta Iran ta shammaci Amurka, ta kwashe duka na'urori da sindarin kera nukiliya tun kafin ta kai mata hari a cibiyoyi 3.
Kasar Iran ta yi magana kan ɓarnar da hare-haren Isra'ila suka yi mata inda ta ce yaki da Isra’ila ya jawo mummunar barna a cibiyoyin nukiliya na kasar.
Labaran Duniya
Samu kari