Labaran Duniya
Kungiyar gwamnonin Najeriya (NGF) ta yabawa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu bisa hanzarin da ya yi wajen agaza wa Jamhuriyar Benin tare da dakile juyin mulki.
Yunkurin juyin mulki a Benin ya kara shiga jerin juyin mulki da dama da sojoji suka yi a kasashen Afrika. Legit Hausa ta yi bayani game da kasashe 8.
Fadar shugaban kasa a Benin ta yi tsokaci kan yunkurin da sojoji suka yi na kifar da gwamnatin Shugaba Patrice Talon. Ta ce sojojin ba su karbe iko a kasar ba.
Rahoton da Google ya fitar na abubuwan da aka fi bincike a manhajarsa a 2025 ya nuna Sanata Natasha Akpoti ce aka fi karanta labaranta, sai su Muhammadu Buhari.
Daya daga cikin jagororin 'yan adawa a kasar Kamaru, Anicent Ekane ya rasu a hannun sojoji kwanaki bayan Paul Biya ya kama shi saboda wasu zarge-zarge.
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya gana da Bola Tinubu a fadar shugaban kasa kan rikicin siyasar da ta barke bayan juyin mulki a Guinea-Bissau.
Mutanen Utqiagvik a Alaska ba za su sake ganin hasken rana ba tsawon kwanaki 64 bayan fara dogon dare, sakamakon juyawar Duniya da ake samu a shekara.
Hukumar USCIS ta ce ta fara duba yiwuwar kwace damar zama a Amurka ga mutanen ƙasashe “masu matsala”, bisa umarnin Shugaba Donald Trump bayan harbin sojoji.
Gwamnatin Najeriya ta la’anci juyin mulkin soja a Guinea-Bissau, tana cewa matakin ya barazana ga dimokuraɗiyya, tsaro da kwanciyar hankali a yanki baki ɗaya.
Labaran Duniya
Samu kari