Labaran garkuwa da mutane
Rahotanni daga jihar Zamfara sun nuna cewa wasu ƴan uwan amarya sun taru sun kashe ɗan bindiga ɗaya kuma sun kwato bindigu a titin Talatan Mafara zuwa Gusau.
Rundunar ƴan sandan jihar Nasarawa ta kama wasu mutum uku da suka yi wa kawun ɗaya daga cikinsu barazanar garkuwa, suka karɓi fansar Naira miliyan biyu.
Rahotanni sun nuna cewa wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kai farmaki garin Dutse da ke babban birnin tarayya Abuja inda suka yi garkuwa da mutane 5.
An kama wata mata mai shekara 40 da take ‘satar’ kanana yara. NAPTIP ta sashen Benin, ta ce sunan matar da aka kama Ikejimba Maryvianney kuma tana karyar Fasto ce.
Wani luguden wuta da aka yi ya hallaka mutane da-dama a wani kauye da ke jihar Zamfara. Hakimin Dogan Daji a Muradun ya ce mutanensu aka kashe ba 'yan bindiga ba.
Miyagun ƴan bindiga sun kai sababbin hare-hare a kauyukan Batsari da Malumfashi a ranaku daban-daban a makon nan, sun sace mutane da dama a jihar Katsina.
Rahoton da muke samu daga jihar Kaduna ya nuna cewa ƴan bindigan jeji sun farmaki wani kauye a ƙaramar hukumar Birnin Gwari, sun sace gomman mutane.
Mutane uku a kihar Edo sun yi karyar an yi garkuwa da su ne da kuma bukatar kudin fansa. 'Yan sanda sun tabbatar da faruwar lamarin da nasarar cafke su
Wasu tsagerun ƴan bindiga sun yi garkuwa da matafiya 16 a kan titin Abuja zuwa Lokoja, sun kuma kashe direba amma an ce 6 daga ciki sun shaki iskar ƴanci.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari