Labaran garkuwa da mutane
Ana fargabar wasu ƴan bindiga da ba a san ko su waye ba sun yi awon gaba da kwamishinan matasa na jihar Anambra tare da mai ɗakinsa ahanyar zuwa Abuja.
Rundunar ƴan sanda reshen jihar Ogun ta tabbatar da cewa an yi garkuwa da waus mutum biyu ƴan ƙasar China, kuma maharan sun fara tuntuɓa domin neman fansa.
Wasu miyagun 'yan ta'adda sun yiwa dakarun sojojin Najeriya kwanton bauna a jihar Sokoto. 'Yan ta'addan sun hallaka sojoji hudu a harin da suka kai.
Masu garkuwa da ɗaliban jami'a da hadiman shugaban ƙaramar hukumar Kabba/Buhu a jihar Kogi sun nemi N10m a matsayin kun fansa, sun sauko daga N100m.
Wasu miyagun ƴan bindiga sun shiga har cikin gida, sun yi awon gaba da wani malami, Sheih Isma'il Gausi a Zaria da ke jihar Kaduna da daren ranar Laraba.
Rahotanni daga yankin karamar hukumar Kajuru a jihar Kaduna sun nuna cewa ɓarayin daji sun hallaka Magajin Garin Gefe da ke yankin Kufana da tsakar dare.
Yan bindiga sun yi ajalin mutane shida, sannan sun yi awon gaba da wasu mutane 26 a hare-haren da suka kai kauyuka huɗu a karamar hukumar Kauru ta Kaduna.
Hukumar da ke kula da harkokin matasa masu yiwa ƙasa hidima a Najeriya NYSC ta ayyana ɓatan kodinetan da ke kula da jihar Akwa Ibom tare da direbansa.
Yayin da rashin tsaro ya ke kamari, an gano yadda gwamnatin tarayya ta fitar da kudi masu nauyi domin yakar ta'addanci a sassan da ta'addanci ya yi katutu.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari