Labaran garkuwa da mutane
Yan sanda sun yi gumurzu wajen ceto matafiya 19 da aka sace a jihar Neja. Matafiyan sun fito ne daga jihar Sokoto zuwa Bayelsa kuma an mayar da su gida.
Kakakin majalisar dokokin jihar Neja ya tabbatar da cewa ƴan bindiga sun sace mutane 22 da suka tare motoci biyar a titin zuwa Kontagora ranar Alhamis.
Shugaban kungiyar likitoci masu neman kwarewa NARD ta ƙasa, Tope Zenith Osundara, ya tabbatar da dawowar likitar da aka yi garkuwa da ita tun Disamɓa.
Yan bindiga dauke da makamai sun kai hari kan wani dan kasuwa a jihar Ebonyi. Yan bindigar sun harbe dan kasuwar tare da ƙona gawarsa a cikin gidansa.
Maharan da suka yi garkuwa da limamin coci a jihar Edo sun tuntuɓi ƴan uwansa sun bukaci lale masu kudi fansa Naira Miliyan 200 kafin da su sake shi.
Wani limamin cocin katolika, Rabaran Tsomas ya nuna halin dattako, inda ya mika kansa ga ƴan bindiga domin su saki ɗalibai 2 da suka yi garkuwa da su a Edo.
Rundunar 'yan sandan jihar Delta, ta sanar da cewa ta samu nasarar cafke wani tsohon kansila kan yunkurin yin garkuwa da mutane. Ta ce ana ci gaba da bincike.
Wasu miyagun ƴan bindiga da ba a san ko su waye ba suns sace limamim cocin St. James’ Parish da ke Awkuzu a jihar Anambra, rundunar ƴan sanda ta ce bata da masaniya.
Jami'an rundunar 'yan sandan Najeriya da ke jihar Plateau sun fafata da masu garkuwa da mutane. 'Yan sandan sun yi nasarar ceto wani matashi da aka sace.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari