Kasashen Duniya
Gwamnatin Amurka na shirin hana jakadun Iran sayayya a wasu manyan shagunan kasar yayin da za su je taron majalisar dinkin duniya na 2025 a Satumba.
Sabuwar annobar cutar Ebola da ta bulla a DR Congo ta kashe mutane 15, WHO ta ce tana aiki cikin gaggawa tare da amfani da rigakafin Ervebo domin dakile cutar.
Kasar Faransa ta dawo da kokon kawunan wasu sarakuna daga kasar Madagascar bayan shafe shekaru 128 da aka kashe su lokacin mulkin mallaka a kasar.
A labarn nan, za a ji cewa kasar Burkina Faso da ke a karkashin mulkin soja ta haramta duk wata alakar soyayya ko aure a tsakanin jinsi daya, ta fitar da hukunci.
Duk da cewar Yammacin duniya irin su Amurka na da tasiri, saurin karuwar jama’a a Afirka da Asiya na kokarin sauya cibiyar tasirin Kiristanci zuwa Kudancin duniya.
Wani luguden wuta na bam daga sojojin Isra’ila ya kashe Firaministan Houthi mai ikirari, Ahmed Ghaleb Nasser al-Rahawi, da wasu jami’an ƙungiyar Houthi a Sanaa.
An hallaka tsohon kakakin majalisar dokokin Ukraine, Andriy Parubiy, a Lviv, abin da ya tayar da hankula a kasar, yayin da shugabanni ke aika wa da sakon ta’aziyya.
Yayin da ake shirin gudanar da taron Majalisar Dinkin Duniya (UNGA) a watan Satumbar 2025, kasar Amurka ta hana shugabannin Falasɗinu shiga taron a New York.
Kotun Equatorial Guinea ta yanke wa Ruslan Obiang Nsue, dan shugaban kasa, hukuncin shekara shida bayan samunsa da laifin sayar da jirgin gwamnatin kasar.
Kasashen Duniya
Samu kari