Jihar Kaduna
Jami'an gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu sun hallara jihar Kaduna domin bayani kan nasarorin shugaban kasar a shekara biyu. Za su fadi ayyukan da aka yi a Arewa.
Reshen jam'iyyar SDP a jihar Kaduna ta ce bata san da maganar kori Nasir El-Rufa'i daga jam'iyyar na tsawon shekara 30. SDP a Kaduna ta ce yana cikin jam'iyyar.
A labarin nan, za a ji cewa iyalan marigayi tsohon shugaban Najeriya sun bar gidansu da ke Daura a Katsina, sun koma gidansa na Kaduna kwanaki da yi masa sutura.
A labarin nan, za a ji cewa tsohon mataimakin ɗan takarar gwamna a jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kaduna ya ce akwai tarin matsaloli, saboda haka ya bar jam'iyya.
Yan bindiga sun kai wani hari yayin da suka sace wani Fasto da wasu biyu a gonarsu da ke Bauda a Maro da ke cikin Karamar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.
Jam'iyyar SDP mai adawa a Najeriya, ta nesanta kanta da Nasir El-Rufai, tana cewa ba mamba ba ne, kuma baya da izini ya wakilci jam’iyyar ko magana da sunanta.
Wasu 'yan bindiga sun kai hari kan makiyaya a jihar Kaduna. An kai hari kan Fulani makiyaya a karamar hukumar Igabi. Ana cigaba da nemo wadanda suka kai harin.
Fusatattun matasa sun toshe hanyar Kano zuwa Zaria na kusan sa’a guda domin nuna fushi kan yadda motocin banki suka buge mutane suka gudu ba tare da taimako ba.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba 'yan Najeriya tabbacin cewa gwamnatinsa na daukar batun yaki da ta'addanci da 'yan bindiga da matukar muhimmancin gaske.
Jihar Kaduna
Samu kari