Jihar Kano
Sarki Muhammadu Sanusi II zai jagoranci hawan babban daki a jihar Kano bayan dawowa daga London. Hakan na zuwa ne bayan sarki Aminu Ado ya tafi Kaduna.
Gwamnatin jihar Kano ta gano yadda ake karkatar da kudade a tsarin biyan albashin ma'aikatan kananan hukumomi. Ta ce za ta dauki mataki kan masu laifin.
NNPP ta yi magana kan zaben 2027 inda mai magana da yawunta, Ladipo Johnson, ya ce suna nazarin yiwuwar ci gaba da zama a NNPP ko kuma shiga kawance da Atiku.
Gwamnatin Edo ta musa zargin IPOB na cewa ta biya iyalan Hauswan da aka kashe a Uromi diyyar Naira biliyan 6. Gwamnan ya ce labarin ba gaskiya ba ne.
Yayin da ake dakon hukuncin kotu kan rigimar masarautar Kano, Aminu Ado Bayero ya yabawa Shugaba Bola Tinubu bisa kafa hukumar raya kiwo da makiyaya ta kasa.
Ana zargin wani matukin tirela da wurgo wani dan Karota da ya shiga motar shi domi duba takardun kayan da ya dauko. Lamarin ya faru wajen gadar Muhammadu Buhari.
A cikin watan Afrilu kadai, an yi yunƙurin kutse gidan Kashim Shettima, an yi zargin hana shi shiga Villa, sannan an yi zargin rikici ya balle a kan idonsa.
Bayan gwamnan Delta ya shiga APC, shugaban jam'iyyar na ƙasa, Abdullahi Ganduje, ya ce wasu gwamnoni daga PDP za su sauya sheƙa zuwa cikinta kafin zaɓen 2027.
Jam'iyyar NNPP reshen jihar Kano, ta nuna rashin damuwarta kan sauya shekar da Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila, ya yi zuwa APC mai adawa a jihar.
Jihar Kano
Samu kari