Jihar Kano
Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya kai ziyara ta musamman ga Muhammadu Sanusi II a fadarsa da ke birnin Kano inda ya ce jihar na da muhimmanci a siyasa.
Tsohon Sakataren gwamnatin Kano, Baffa Bichi ya zargi NNPP da fifita kansu a maimakon talakawa, ya ce shakar mutuwa ce ta sa suka fice daga jam’iyyar.
Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero ya yi sabon nadi a masarautarsa. Sarkin ya nada yayansa Sanusi Ado Bayero a matsayin sabon Galadiman Kano.
Yayin da Sarki Muhammadu Sanusi II ya yi hawan Babban Daki, Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya halarci taron sarakunan Arewa da aka gudanar a birnin Kaduna.
Dattijo kuma jarumin Kannywood, Malam Inuwa Ilyasu, ya bayyana cewa ya shiga harkar fim ne domin fadakar da jama'a da kuma koyar da addinin Musulunci.
Sarki Muhammadu Sanusi II zai jagoranci hawan babban daki a jihar Kano bayan dawowa daga London. Hakan na zuwa ne bayan sarki Aminu Ado ya tafi Kaduna.
Gwamnatin jihar Kano ta gano yadda ake karkatar da kudade a tsarin biyan albashin ma'aikatan kananan hukumomi. Ta ce za ta dauki mataki kan masu laifin.
NNPP ta yi magana kan zaben 2027 inda mai magana da yawunta, Ladipo Johnson, ya ce suna nazarin yiwuwar ci gaba da zama a NNPP ko kuma shiga kawance da Atiku.
Gwamnatin Edo ta musa zargin IPOB na cewa ta biya iyalan Hauswan da aka kashe a Uromi diyyar Naira biliyan 6. Gwamnan ya ce labarin ba gaskiya ba ne.
Jihar Kano
Samu kari