Jihar Kano
Bayanan da muke samu yanzu sun tabbatar da cewa masarautar Kano ta tabbatar da rasuwar Sarkin Gabas, Hakimin Kabo, Alhaji Idris Muhammad Adamu DanKabo.
Saudiyya ta saki mahajjatan Najeriya uku da aka tsare bisa zargin safarar kwayoyi bayan NDLEA ta gano masu laifin a Kano. Sa bakin Tinubu ya tabbatar da sakin su.
Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bayyana cewa an fara ganin ribar kula da gwamnatin Abba Kair Yusuf ke yi da bangaren ilimi bayan fitowar sakamakon NECO.
A labarin nan, za a ji cewa gwamnatin Bola Tinubu ta fara neman share hawayen hukumar asibitin koyarwa a asibitin Aminu Kano bayan ta fito rokon KEDCO a jaridu.
Sanata Barau Jibrin ya karbi matasan NNPP da Kwankwasiyya da suka fito daga Danbatta zuwa jam'iyyar APC a Abuja. Barau ya ce NNPP ta kusa rushewa a Najeriya
NiMet ta gargadi ‘yan Najeriya kan yiwuwar saukar ruwan sama da iska mai karfi a jihohi da dama, ta ba da shawarwari don kariya daga haɗurra da ambaliya.
Gwamnatin Kano ta bayyana farin cikinta kan yadda jihar ta zama ta daya a jerin jihohin da suka fi cin jarabawar NECO da aka saki ranar Laraba, 17 ga watan Satumba.
Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA), ta sanar da cewa hukumomi a Saudiyya sun sako maniyyatan Najeriya da aka tsare a kasar.
A labarin nan, za a ji cewa hukumar ICPC ta samu nasara a kotu bayan wasu jami'an gwamnatin Kano sun kai ta kotu domin hana ta gudanar da binciken tallafin karatu.
Jihar Kano
Samu kari