Jihar Kano
An kama wasu 'yan daba da suka yi shigar mata domin kai zafafan hare hare yankunan Kano da nufin kisan gilla. An kama su a unguwar Kurna da ke Kano.
Fitaccen jarumi a masana'antar Kannywood, Tahir Muhammad Fagge, ya yabawa Ali Nuhu kan gudunmawar da yake ba shi musamman yadda yake fama da jinya.
Gwamnatin tarayya ta gargadi yankuna 32 a jihohi 11 kan yiwuwar ambaliya daga Satumba 14–18, yayin da kogunan Benue, Niger da Gongola suka fara cika ruwa.
Dr. Maryam Shetty ta kammala gasa ta farko ta karatun Alƙur’ani a Kano, inda Nuraddeen Mu’azu ya zama zakara, kuma ya samu N1m, yayin da aka yi addu’ar zaman lafiya.
NiMet ta yi hasashen ruwan sama mai karfi zai sauka a jihohi 15 na Arewacin Najeriya a ranar Lahadi, tare da gargadi ga jama’a, direbobi da kamfanonin jiragen sama.
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya yi magana an yadda ake samun lalatattun shugabanni a Najeriya inda ya shawarci matasa su yi kokarin kwace mulki a kasar.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya tura kudiri a gaban majalisar dokoki kan auren jinsi. Kudirin ya kuma shafi munanan dabi'u na madigo da liwadi.
Tawagar 'yan Najeriya mazauna Faransa sun ba Sanata Rabiu Musa Kwankwaso lambar yabo saboda yadda ya ke tallafawa mutane da tallafin karatu a Kano.
A labarin nan, za a ji cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar ya bayyana cewa akwai bukatar a tabbatar wa kananan hukumomin yancin kansu don kawi ci gaba.
Jihar Kano
Samu kari