Jihar Kano
Wasu masu ruwa da tsakin APC a Kano sun hango cewa ba za a masu adalci ba idan jagoran NNPP, Rabiu Kwankwaso ya sauya sheka tare da Gwamna Abba Kabir.
An gurfanar da malamin Musulunci, Sheikh Ibrahim Isa Makwarari a kotun Kano kan zargin karkatar da filayen gwamnati da na al'umma. Ana zargin shi da laifuffuka.
A labarin nan, za a ji cewa rundunar yan sadan jihar Kano ta zargi makotan Fatima Abubakar da ta gamu da iftila'i da yaranta da karairayi a shafukan sada zumunta.
Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya kira Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rattaba hannu kan hukuncin kisa don rage kisan kai a jihar, yana jaddada adalci da tsaro.
Dan siyasa Aminu Lawal Sufi ya bayyana damuwa akan dambarwar siyasar Kano da rabuwa da Rabiu Kwankwaso, yana jaddada hakan alheri ne ga Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya ce har yanzu Abba Kabir Yusuf bai yanke matsaya kan sauya sheka ba amma ana tattaunawa.
Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II, ya koma karatun digiri a Jami'ar Northwest, yana karatu a fannin shari’a, tare da jawo farin ciki tsakanin dalibai.
Shugaban APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas ya bayyana cewa ko da SanatanKwankwaso ya sauya sheka zuwa jam'iyyar ba zai yiwu ya zama shi ne jagora ba.
Jam'iyyar APC ta bayyana cewa kodayake ta tsaya a kan doron dimokiraɗiyya wajen shirin tunkarar zaben 2027 mai zuwa, gwamnonin da ke shigowa cikinta na da alfarma.
Jihar Kano
Samu kari