Isra'ila
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi magana kan tattaunawa inda ya ce kasar ba ta neman tsagaita wuta, sai dai cikakken tsarin kawo karshen yaki.
Ministan tsaron kasar Isra'ila, Israel Katz ya ce kasar na shirin mamaye wasu yankunan kudancin Lebanon ko bayan yaki da Hezbollah yayin da ake yaki da Iran.
Rundunar dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC), ta kaddamar da hare-hare kan Amurka da Isra'ila a yankin Gabas ta Tsakiya yayin da ake yaki.
Fadar White House ta bayyana cewa shugaban Amurka zai so kasashe Larabawa su biya shi makudan kudin da ya kashe a yaki da kasar Iran da ya kai hare-hare.
Dakarun sojojin Iran sun samu nasarar kakkabo jirgin leken asiri na MQ-9 da ke da alaka da kasashen Amurka da Isra'ila, an ce jirgin yana da matukar tsada.
Shugaban Amurka, Donald Trump ya fadawa hadimansa cewa yana son kawo karshen yakin Iran ba tare da bude mashigar Hormuz ba duk da ya nemi haka a baya.
Wata kungiyar Musulunci a Najeriya ta bukaci gwamnatin tarayya karkashin Bola Tinubu ta yanke alaka da Isra'ila tare da tir da Amurka kan yakin da ake da Iran.
Mayakan kungiyar Hezbollah sun gwabza fada da sojojin Isra'ila a Kudancin Lebanon. Mayakan na Hezbollah sun samu nasarar hallaka sojojin Isra'ila.
Gwamnatin Iran ta sake karyata kalaman jami'an Amurka, wadanda suka yi ikirarin an fara zaman tattaunawa domin kawo karshen yakin Gabas ta Tsakiya.
Isra'ila
Samu kari