Isra'ila
Shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron ya bayyana cewa karfin soji ba zai iya warware matsalar shirin nukiliyar Iran ko bude mashigar ruwa ta Hormuz ba.
Kasashen da musulmi suka fi rinjaye ciki har da Saudiyya da Masar sun nuna adawada dokar hukuncin kisa da Isra'ila ta amince da ita kan Falasdinawa.
Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta tabbatar da cewa ta samu sako kan batun tsagaita wuta ta hannun masu shiga tsakani, ta ce za ta yi nazari a kai tukunna.
Sani Buhari, wanda aka fi sani da Sarki Waspapping ya musanta zargin da ake cewa NSA je ya tura aka kama shi kan maganar da ya yi game da yakin Iran da Isra'ila.
Hukumomin agajin gaggawa na Isra'ila sunn tabbatar da cewa akalla mutane 14 ne suka samu raunuka sakamakon harin makami mai linzami a kusa da birnin Tel Aviv.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya ce shugaban Iran yana neman tsagaita wuta, duk da sabanin kalamansa kan dakatar da yakin ko kara tsananta shi.
Rundunar IRGC ta kasar Iran ta ƙaddamar da gagarumin harin ramuwar gayya da makamai sama da 300 kan sansanonin sojin Amurka da Isra'ila a yau Laraba.
A labarin nan, za a ji cewa rahotanni sun tabbatar da yadda ake samun karuwar rasa rayuka yayin da makaman da Iran ke harba wa ke yi wa Isra'ila illa.
Kasar Iran ta ce ta harbo jirgin sama mara matuki na Amurka nau’in “LUCAS” a Khorramabad yayin da ake ci gaba da yaki da Isra'ila a Gabas ta Tsakiya.
Isra'ila
Samu kari