Jihar Gombe
Malamin addini ya fadi hukuncin tuban yan ta'adda da yan bindiga irinsu Bello Turji. Malamin ya ce idan Bello Turji ya tuba za a karbi tubansa a Musulunci.
Ana hasashen 'Hamster' na shirin fashewa, asibitin Gwamnatin Tarayya (FTH) da ke Gombe ya haramtawa ma'aikata 'kirifto' da 'mining' yayin da suke bakin aiki.
Rikicin cikin gida a jam'iyyar NNPP ya kara ƙamari yayin ake zargin wasu jita-jiganta a jihohi biyar da yi mata zangon-kasa inda ta kaddamar da fara bincikensu.
Rundunar tsaro ta bukaci al'umma da su guji yin martani kan lamarin Burgediya janar MS Adamu game da sojan ruwa, Abbas Haruna kan zargin cin zarafinsa.
Bayan duba irin barnar da ambaliyar ruwa ta yi a Maiduguri, Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa ya ba gwamnatin Borno tallafin N50m da jiragen ruwa.
Kungiyar malaman jami'a reshen jihar Gombe ta shiga yajin aiki kan gaza cika alkawarin gwamnati. Kungiyar ASUU ta ce gwamnatin Gombe ne ta jawo yajin aikin.
Sheikh Muhammad Adamu Dokoro ya ce Fir'aunanci da ake a Najeriya ya yi yawa bayan kara kudin man fetur. Malamin ya ce yan siyasa ba sa tausayawa talaka.
Kungiyar gwamnonin Arewacin Najeriya ta yi Allah wadai da harin da 'yan ta'adda suka kai a jihar Yobe wanda ya yi sanadiyyar hallaka rayukan mutane masu yawa.
Gwamnonin Arewa sun fitar da matsaya kan matsalar tasro domin kawo karshen yan bindiga da suka addabi yankin. Gwamna Inuwa Yahaya ne ya yi bayani.`
Jihar Gombe
Samu kari