Labaran kasashen waje
Sojojin Amurka sun kwashe yanasu-yanasu sun bar sansanoninsu zuwa otal-otal a Gabas Ta Tsakiya sakamakon luguden wutar Iran, yayin da Tehran ke farautar su.
Rundunar tsaron Isra'ila (IDF), ta bayyana cewa ta hallaka daya daga cikin manyan kwamandojin Iran. Isra'ila ta hallaka kwamandan sojojin ruwa na rundunar IRGC.
Shugaba Donald Trump ya yi watsi da shawarar Benjamin Netanyahu na kiran al'ummar Iran su fito zanga-zanga, yana tsoron hakan zai kai ga "zubar da jini."
Firayim Ministan Malaysia, Anwar Ibrahim, ya goyi bayan yunƙurin Pakistan na shiga tsakanin Amurka da Iran domin samar da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.
Firaministan kasar Spain, Pedro Sanchez, ya ragargaji Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu. Ya bayyana cewa yana da mugun nufi kan kasar Lebanon.
Iran na ci gaba da harba makamai masu linzami kan Isra'ila yayin da ake ci gaba da fafatawa a Gabas ta Tsakiya. Makaman na Iran sun yi barna a wasu birane.
Harin makami mai linzami da Iran ta kai Tel Aviv a ranar 24 ga Maris ya kashe aƙalla mutane 16, tare da ruguza gine-gine da jikkata wasu da dama.
Tarayyar Turai (EU) da Najeriya sun amince su faɗaɗa haɗin gwiwa kan hakar ma'adanai, tsaro, da kasuwanci yayin da ake fama da yaki a Gabas ta Tsakiya.
Yarima Mohammed bin Salman ya matsa wa Donald Trump lamba domin ya ci gaba da yaƙi da Iran, inda ya bayyana lamarin a matsayin "dama" ga yankin Gabas ta Tsakiya.
Labaran kasashen waje
Samu kari