Gobara
An samu tashin wata gobara a kasuwar Katako da ke birnin Enugu, babban birnin jihar Enugu a ranar Talata. Shaguna biyar da ke cikin kasuwar sun kone.
An shiga takaici a jihar Lagos bayan zuciyar wata ‘yar kasuwa, Alhaja Iyabo ya buga, wanda ya yi sanadiyyar rasuwarta saboda rushe shagonta da N50m a ciki.
A safiyar yau ne wata mota dauke da man fetur ta fadi kuma ta kama da wuta a yankin Ibafo/Aseese dake babban titin Lagos zuwa Ibadan, amma an shawo kan matsalar.
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya mika tallafin N5.3m ga wadanda iftila'in harin masallaci ya rutsa da su a garin Gadan dake Kano.
An samu tashin gobara a sakatariyar gwamnatin jihar Kaduna wacce ta tafka barna mai yawa. Gobarar ta shafi wasu ofisoshi da ke wajen sannan ta lalata su.
Dalibi daya ya mutu, sannan an lalata kadarori da dama a lokacin da gobara ta tashi a makarantar Bishop Crowther Memorial, Awka, babban birnin jihar Anambra.
Hukumar kare afkuwar hadurra ta kasa (FRSC) ta gargadi masu ababen hawa kan daukar fetur a cikin jarkoki idan suna tafiya. Hukumar ta ce hakan zai haddasa gobara.
Wata gobara ta tashi a gidan tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau a cikin daren ranar Lahadi. Gobarar ta lalata wani daki a cikin gidan.
Rikicin daba a jihar Lagos ya jefa jama'a cikin fargaba bayan sun tasamma kona wata kasuwa. Har yanu jami'antsaro ba su iya kwabtar da tarzomar ba.
Gobara
Samu kari