Yaki da ta'addanci a Najeriya
Wasu bama-bamai da 'yan ta'adda suka dasa a kan hanya a jihar Borno sun yi sanadiyyar salwantar da rayukan mutum 11 tare da raunata wasu mutanen daban.
Hedkwatar tsaro ta kasa (DHQ) ta sanar da adadin 'yan ta'addan da sojoji suka hallaka a cikin watan Afirilu tare da adadin mutanen da aka ceto wadanda aka sace.
Tsagerun ƴan bindiga sun kai farmaki kan matafiya a babban titin Abuja zuwa Kaduna, sun kashe wani direba sannan sun tafi da mutim biyu zuwa cikin daji.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu tsagerun ƴan bindiga da ake kyautata zaton fulani makiyaya ne sun yi ajalin mutum uku a kauyen Nimbo da ke jihar Enugu.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce sojoji ba za su yi ƙasa a guiwa ba har sai sun ga bayan duk wani nau'in ta'addanci a faɗin ƙasar nan domin zaman lafiya ya samu.
Rundunar sojojin ƙasa ta Najeriya ta bayyana cewa dakarunta sun yi nasarar kashe ƴan ta'adda uku, sun kamo biyu sannan sun kwato makamai a Sokoto, Kaduna da Filato.
Rundunar sojin Najeriya ta gano wurin da 'yan ta'adan ISWAP ke hada burodi a jihar Borno. Sojojin sun lalata wurin tare da sauran kayan hada burodin
Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa dakarunta da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Arewa maso Gabas sun halaka ƴan ta'adda biyu a jihar Borno.
Mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaron ƙasa (NSA), Malam Nuhu Ribaɗu ya bayyana cewa Najeriya za ta bi hanyoyin zama wajen kawar da ta'addanci a ƙasar.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari