Yaki da ta'addanci a Najeriya
Hedkwatar tsaron Najeriya ta bayyana wasu mutum tara da take nema ruwa a jallo a Arewa maso Gabas kan zargin ta'addanci da rikau, ta lissafo sunayensu.
Hedkwatar tsaro ta ƙasa watau DHQ ta bayyana cewa dakarun sojoji sun yi nasarar kashe ƴan ta'adda 481, sun kubutar da mutane 492 da aka yi garkuwa da su.
Wasu mahara da ake kyautata zaton ƴan bindiga nw sun hallaka matasa uku a yankin ƙaramar hukumar Barkin Ladi jiya Laraba, sun kuma lalata gonakin mutane.
Dakarun tsaron sa kai na jihar da aka fi sani da Askarawa sun yi artabu da yan ta’adda da su ka yi kokarin kai hari karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.
Rundunar ƴan sanda reshen jihar Imo ta tabbatar da fashewar bom a kasuwar Orlu ta ƙasa da ƙasa da ke jihar Imo, ta ce miyagu 2 da suka dasa shi sun mutu.
Wasu miyagu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun je har gona sun kashe manomi da ƴaƴansa guda biyu a yankin karamar hukumar Ivo ta jihar Ebonyi.
Rundunar sojojin Najeriya ta ce dakarunta sun yi nasarar kama wani jagoran ƴan bindiga, Abubakar Ibrahim wanda aka fi sani da Habu Dogo a jihar Sakkwato.
Kakakin majalisar dokokin jihar Neja ya tabbatar da cewa ƴan bindiga sun sace mutane 22 da suka tare motoci biyar a titin zuwa Kontagora ranar Alhamis.
Hedkwatar tsaron Najeriya watau DHQ ta musanta ikirarin majalisar dokokin jihar Neja cewa ƴan ta'adda sun kwace sansanin ɗaukar horon sojoji a Kontagora.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari