Yaki da ta'addanci a Najeriya
Hukumar ƴan sandan Najeriya ta gayyaci shugaban ƙungiyar kwadago ta ƙasa, Joe Ajaero kan zarge-zarge da suka haɗa da ɗaukar nauyin ta'addanci da sauransu.
Miyagu sun hana mazauna kananan hukumomi biyu; Musawa da Kankia a jihar Katsina sakat, yayin da su ka kai hari tare da sace mata da yara da magidanta.
Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta bijiro da wata manhaja mai suna mobilizer da za ta ba wa yan kasa damar mika sakon ta'addanci ko rashin tsaro a yankunansu.
Basarake a Takum da ke jihar Taraba, Barista Sopiya Ahmadu Gboshi ya nuna damuwa kan rasa rayuwa a yankin inda ya zargi yan jihar Benue da kara rashin tsaro.
Matafiya sun yi kicibis mugun gamo da 'yan ta'adda hanyar Gusau-Funtua, inda miyagun su ka ɗauke fasinjojin mota uku,tare da sace wasu a Unguwar Chida.
Rundunar sojojin ƙasa ta Najeriya ta bayyana cewa ƴan ta'adda biyar sun baƙunci lahira yayin da dakaru suka kai samame sansanin ISWAP a Bama da ke jihar Borno.
Yan bindiga sun yi ajalin mutane shida, sannan sun yi awon gaba da wasu mutane 26 a hare-haren da suka kai kauyuka huɗu a karamar hukumar Kauru ta Kaduna.
Yayin da rashin tsaro ya ke kamari, an gano yadda gwamnatin tarayya ta fitar da kudi masu nauyi domin yakar ta'addanci a sassan da ta'addanci ya yi katutu.
Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana dumbin nasararo da dakarunta suka samu kan ƴan ta'adda, ƴan bindiga da sauran miyagu a faɗin kasar nan a watan Yuli.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari