Yaki da ta'addanci a Najeriya
Hadimin shugaba Donald Trump, Massad Boulos ya karyata cewa ana yi wa kiristoci kisan kare dangi a Najeriya. Ya ce an fi kashe Musulmi a kan Kiristoci.
Rikici tsakanin masu hakar ma’adanai da ‘yan bindiga a Birnin Gwari, ya yi sanadin mutuwar mutane 7, yayin da mazauna suka bukaci gwamnati ta dauki mataki.
A labarin nan, za a ji cewa gwamnatin jihar Kebbi ta baza komarta zuwa kasar Sin domin ta fatattaki Lakurawa a kokarinta na dawo da zaman lafiya sassan jihar.
Rundunar tsaron Najeriya ta bayyana shirin murkushe kungiyar 'yan ta'addan Wulowulo da aka ce tsagin Boko Haram ne da ta bulla a Arewa ta Tsakiyan Najeriya.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bukaci ƙara yawan addu’o’i domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar baki daya yayin ganawa da malaman Musulunci.
Reno Omokri ya karyata zargin cewa gwamnatin Najeriya na tallafa wa Boko Haram, ya kalubalanci Sanata Ted Cruz ya kawo hujjoji da shaidun zancensa.
Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa, ya gargadi jama'a kan bullar kungiyar da ya yi zargin wani ɓangaren Boko Haram ne da suka kwararo yankin
’Yan sanda sun hana ‘yan bindiga kai hari a dajin Byazhin, da ke birnin tarayya Abuja, sun kwato bindigar AK-47 da alburusai 30, sun kuma kara tsaurara tsaro a FCT.
A labarin nan, za a ji cewa an yi ba ta kashi a tsakanin sojojin Najeriya da miyagun 'yan bindiga jim kadan bayan an kammala yarjejeniyar zaman lafiya a Katsina.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari