Gwamnatin tarayyar Najeriya
Rufe matatar man Fatakwal ya haddada cece kuce tsakanin masana da masu ruwa da tsaki a harkar kan fetur, an ci gaba da kira ga gwamnati ta sayar da matatu.
Majalisar Wakialai ta ƙarya ikirarin wani jigon APC cewa tun da Bola Tinubu ya karɓi mulki, kowane ɗan Majalisar Wakilai na samun N1bn kudin ayyukan mazaɓa.
Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ya bayyana cewa yana da shejsra 10 a duniya aka kashe mahaifinsa lokacin wani rikicin addini a jihar Kaduna a 1992.
Shehu Atiku Abubuwa ya zargi gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da shirin kinkimo bashin Naira tiriliyan 40 domin amfani da su wajen yakin neman zabe a shekarar 2027.
NiMet ta yi hasashen saukar mamakon ruwa a jihohi 14 daga 28 zuwa 30 ga Mayu, ta yi gargadin yiyuwar afkuwar ambaliya da iska mai karfi. An ce jihohi sun fara shiri.
Nyesom Wike ya ce kin biyan haraji da mazauna babban birnin tarayya ke yi na hana ci gaba a Abuja, ya kuma lashi takobin kwace kadarorin da ba a biya wa haraji ba.
Wani gini mai hawa biyu ya rushe a Ikorodu, Legas, inda ya hallaka mutum uku. LASEMA ta ceto mutum tara, ta kuma fara rushe ginin gaba ɗaya don kare lafiyar jama'a.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi murnar cika shekara 60 a duniya, ya tuna gudummawar da ya bai wa Najeriya.
Wata kotun laifuffuka a jihar Legas ta yanke wa ɗan tsohon shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa, Mamman Ali, hukuncin ɗaurin shekaru 14 a gidan gyaran hali.
Gwamnatin tarayyar Najeriya
Samu kari