Yan bindiga
Rahotanni sun bayyana cewa wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da wasu Fastoci guda shida a jihar Abia. Sun dai yi garkuwa da su ne kan hanyarsu ta zuwa wa'azi.
Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi ya sha alwashin sanya hannu a dokar kisan kai ga masu ba 'yan bindiga bayanan sirri wanda suke cutar da al'umma.
Rahotanni sun nuna cewa 'yan bindiga sun yi wa jami'an tsaron jihar Zamfara kwanton bauna a karamar hukumar Maradun. Sun hallaka jami'ai guda uku.
'Yan bindiga sun yi ajalin mutane 24 wadanda mafi yawansu 'yan banga ne a karamar hukumar Sabuwa da ke jihar Katsina a daren ranar Alhamis 2 ga watan Mayu.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai harin ta'addanci a karamar hukumar Makarfi ta jihar Kaduna inda suka hallaka wani Dagaci tare da bankawa gidansa wuta.
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kare matakin gwamnonin Arewa na zuwa kasar Amurka taro kan matsalar rashin tsaron da ta addabi yankin.
Wasu hatsabiban 'yan bindiga sun sake kai mummunan hari a karamar hukumar Birnin Gwari a Kaduna inda suka sace Dagatai biyu da hallaka 'yan banga takwas.
Ministan Abuja ya nemi hadaka da kasar Hungary domin inganta noma da tsaro a birnin tarayya. Ya yi jawabin ne yayin wata ziyara da ya kai ofishin jakadancin kasar.
Rahotanni sun nuna cewa wasu da ake kyautata zaton ‘yan ta’addan Boko Haram ne da suka tuba sun kona shingayen binciken kwakwaf na hukumar NDLEA da kwastam a Borno.
Yan bindiga
Samu kari