Yan bindiga
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari makarantar sakandare ta Kiri a Kogi, inda suka kashe mutum biyu, amma gwamnati ta tabbatar cewa ba a sace ɗalibi ko guda ɗaya ba.
Wata mota ta zubar da tarin harsashi a kusa da kofar shiga jami'ar ABU Zariya. Ana zargin cewa motar za ta wuce Katsina ne kuma an mika harsashin ga jami'an tsaro.
Dakarun Operation zafin wuta sun kai wani gagarumin farmaki kan 'yan ta'adda a jihar Taraba. Sojoji sun samu nasarar fatattakar 'yan ta'addan bayan shiga maboyarsu.
Shugaban CAN na Arewa, Rabaran John Hayab, ya ce wani uba mai yara uku da aka sace a makarantar St Mary’s a Niger, ya mutu sakamakon bugun zuciya.
Tsohon minista a Najeriya, Solomon Dalung ya zargi Shugaba Tinubu da fallasa muhimman bayanan tsaro a fili, yana mai cewa hakan yana kara wa ’yan ta’adda karfi.
Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Benjamin Kalu ya ce ya zama wajibi a hana tattaunawa da 'yan bindiga masu garkuwa da mutane a Najeriya ko yafe musu.
An gano wani bidiyon da ya fito daga hannun dan bindiga ya nuna yadda aka kula da yaran, tare da bayyana cewa sulhu da tattaunawa ne ya ba da damar sakin daliban.
Rundunar ’yan sandan Kwara ta tabbatar da sace mutane 10 a Isapa, tare da kaddamar da aikin ceto bayan harin da ake zargin makiyaya ne suka kai garin.
Dan majalisar wakilai, Hon. Alhassan Ado Doguwa ya nemi a rufe majalisar wakilai sabida yadda ake zubar da jini a fadin Najeriya sakamakon rashin tsaro.
Yan bindiga
Samu kari