Yan bindiga
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai hare-haren ta'addanci a wasu kauyukan karamar hukumar Shiroro cikin jihar Neja. Sun hallaka mutum bakwai har lahira.
Yan bindiga sun kai hari jihohin Zamfara da Katsina inda suka kashe mutane kimanin 50. Kwamishinan yan sandan jihar Zamfara ya tabbatar da faruwar lamarin.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da nasarar dakile harin garkuwa da ‘yan bindiga a suka kai kan Sarkin Ninzo, Alhaji Umar Musa, a karamar hukumar Sanga.
Hatsabibin ɗan ta'adda, Bello Turji ya fitar da wani sabon faifan bidiyo da ya ke ƙaryata hukumomin Nijar cewa sun cafke mayakinsa, Baleri inda ya nuna shi a bidiyo.
Wasu mutane da ke tserewa harin 'yan bindiga a jihar Neja sun rasa rayukansu a cikin ruwa. Mutanen sun rasu ne bayan kwale-kwalen da suke ciki ya yi hatsari.
Wasu ƴan bindiga sun kai hari fadan sarkin Ninzo a karamar hukumar Sanga da ke jihar Kaduna inda suka yi awon gaba da matarsa a cikin daren jiya Laraba.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai harin ta'addanci a karamar hukumar Bassa ta jihar Plateau. 'Yan bindigan sun hallaka wani fasto tare da wasu mutum hudu a harin.
Gwamnatin jihar Niger ta dora laifin gaza ceto wadanda suka makale a karkashin mahakar ma'adanai kan rashin tsaro da ya addabi yankin Galadima-Kogo.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun hallaka dan Sarkin Hausawan Janjala a karamar hukumar Kagarko da ke jihar Kaduna. An ce budurwar shugabansu ya aura.
Yan bindiga
Samu kari