Zaben Shugaban kasan Najeriya
Kungiyar mata ta AYW ta bayyana Atiku Abubakar a matsayin dan takarar da za ta marawa baya a zaben 2027, tana yabonsa da kwarewa, hangen nesa, da kishin Najeriya.
Atiku da Gudaji Kazaure sun tattauna kan halin da Najeriya ke ciki da matakan ceto ta daga matsaloli, tare da haɗa kai domin samar da jagoranci na gari.
Karamin Ministan gidaje da raya karkara, Yusuf Ata ya caccaki hadakar Atiku Abubakar, Nasir El-Rufa'i da Peter Obi da adawa da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Babban lauya a kasar nan, Mike Ozekhome (SAN), ya zargi gwamnatin tarayya da karya dokar kasa, da kuma gudanar da juyin mulki a jihar Ribas, wanda ya saba doka.
Wani masani mai sharhi kan harkokin siyaaa, Kelly Agada ya ce hogewar El-Rufai wajen iya tara jama'a da kuma ƙulla kawance da manyan ƴan adawa za su taimake shi.
Tsohon ɗan takarar shugaban kasa, Mista Peter Obi ya buɗe shafin TikTok, ya samu mabiya mutane sama da 6,000 cikin ƴan sa'o'i, ya wallafa bidiyo mai ɗauke da saƙo.
Gwamnonin jihohin kasar nan sun fara neman a lallaba shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a kan ya taka burki kan shirin biyan kananan hukumomi kudinsu kai tsaye.
Rahotanni daga fadar gwamnatin jihar Bauchi sun nuna cewa nan ba da jimawa da Peter Obi zai fice daga LP zuwa jam'iyyar PDP a shirye-shiryen 2027.
Jam'iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa maganar cewa akwai shirin sake tsayar da Goodluck Ebele Jonathan takarar shugaban kasa ba ta da tushe ballantana makama.
Zaben Shugaban kasan Najeriya
Samu kari