Kasar waje
'Yan Najeriya masu shiga kasar Nijar da fasfon ECOWAS sun fara fuskantar kalubale da aka fara dakatar da su. Ana zargin ana dawo da wasu zuwa gida Najeriya.
Gwamnati Neja ta gudanar da jarrabawa ga dalibai da ake shirin turasu karatu kasashen waje. Za a tura dalibai 1,000 zuwa kasashen Canada, China, India da Brazil.
Rahotanni da muke samu sun ce tsohuwar Jakadiyar Najeriya a Trinidad da Tobago, Ambasada Nne Furo Kurubo, a jihar Lagos tana da shekara 84 a duniya.
Karamin ministan tsaro a Najeriya, Bello Matawalle ya tsoma baki kan batun hana sojojin Najeriya 'visa' zuwa kasar Canada inda ya ce za su dauki matakin da ya dace.
Bayan caccakar Canada da Nuhu Ribadu ya yi, ofishin jakadancinta a Najeriya ya mayar da martani kan rahotannin hana hafsan tsaron Najeriya shiga kasar.
Majalisar Turai ta bukaci Najeriya ta saki Yahaya Sharif-Aminu tare da soke dokokin hukunta masu batanci da suka saba wa yarjejeniyoyin kasa da kasa da kundin mulki.
Shugaba Tinubu ya isa Addis Ababa domin halartar taron kungiyar AU daga 14 zuwa 18 ga Fabrairun 2025, inda za a tattauna kan tsaro, kiwon lafiya da ci gaba.
Mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ya soki gwamnatin Canada da ta hana hafsan tsaron Najeriya Christopher Musa shiga kasar da sauran sojoji.
Dauda Kahutu Rarara ya saki waka ta biyu, a jerin wakoki 9 na caccakar shugaban Nijar, Tchiani, yayin da Kosan Waka ya fitar da waka mai kare Tchiani.
Kasar waje
Samu kari