Kasar waje
A labarin nan, za a ji cewa gwamnatin Najeriya ta ce Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya kammala ayyukansa a kasar Japan, kuma zai mika zuwa Brazil.
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ce kasar tana samun ci gaba sosai kuma yana rage matsaloli a karkashin shugabancinsa na shekaru biyu da ya yi.
Yayin da ake fama da matsalar tsaro a fadin Najeriya, Hafsan tsaro, Janar Christopher Musa ya ce bakin da ke shiga kasar suna kara matsalar a yanzu.
Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta tabbatar da rasuwar karamin Jakadan Najeriya a jamhuriyar Kamaru, Taofik Obasanjo Coker, ya mutu ranar Asabar.
Hukumar NIDCOM ta ce ‘yan Najeriya 7,000 sun makale a Libya, yayin da IOM ta kaddamar da sabon tsarin da zai samu taimakon ministoci da gwamnonin jihohi.
Kasar Iran ta bayyana cewa ba ta neman kowa da fada amma a shirye take ta aake fuskantar kasar Isra'ila matukar ta sake kawo mata hari, ta kera makamai.
Hukumomin tsaro a Amurka sun cafke wata mata a kasar da ta yi barazana ga Shugaba Donald Trump a kafar sadarwa ta intanet domin daukar fansar rasa rayuka.
Kungiyar Musulmi a kasar Finland ta yi Allah wadai da kalaman ministar Tsaron Jama’a, Sanni Grahn-Laasonen kan kalamanta game da sanya hijabi a makaranta.
Gwamna Bala Mohammed ya nada ɗan ƙasar China, Li Zhensheng matsayin mai ba shi shawa don jawo masu zuba jari, bunƙasa kasuwanci da gina ababen more rayuwa a Bauchi.
Kasar waje
Samu kari