Arewa
Hedkwatar tsaron Najeriya ta bayyana wasu mutum tara da take nema ruwa a jallo a Arewa maso Gabas kan zargin ta'addanci da rikau, ta lissafo sunayensu.
Rahotanni sun tabbatar da cewa akalla mutane 22 ne suka ce ga garinku nan yayin da wani ramin haƙar ma'adanai ya rufta kansu a yankunan Adamawa, Taraba.
Gwamnatin jihar Kano ta musanta alakar siyasa da kuma sauye-sauyen manyan sakatarori a ma'aikatu da aka yiwa wasu manyan daraktoci da cewa rigimar NNPP ta jawo.
A wannan rahoton za ku ji yadda kamfanonin rarraba hasken lantarki (DisCos) sun sanar da kara kudin lantarki da ake biya ta mita da abokan huldarsu ke amfani da su.
Gwamnatin tarayya ta ce ta gano matsalar da ke jawo yawan lalacewar wutar lantarki a Najeriya bayan kasa ta sake fadawa duhu a karo na 10 a shekarar 2024.
Gwamnatin jihar Kaduna ta tarbi yara 39 da gwamnatin Bola Tinubu ta sako kan zargin tsunduma zanga-zanga inda aka ba su kyautar N100,000 da sababbin wayoyi.
Gwamnonin jihohin Arewa 19 sun yi ta'aziyyar rasuwar hafsan rundunar sojojin ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, wanda ya rasu bayan fama da jinya.
Wasu 'yan bindiga sun datse kan manoma 6 tare da yin awon gaba da kawunan yayin da suka kashe mutane 10 a harin da suka kai jihar Neja. An ce an sace Indiyawa.
Yayan Namadi Sambo, tsohon mataimakin shugaban kasa a mulkin Goodluck Jonathan mai suna Alhaji Sulaiman Sambo ya rasu yana da shekaru 82 a duniya.
Arewa
Samu kari