Arewa
Kotu a Abuja ta amince tsohon gwamnan Taraba, Darius Ishaku damar tafiya kasashen waje don neman magani bayan fuskantar shari'a kan zargin almundahana.
Gwamnatin jihar Kwara ta karrama Alhaji Abubakar Tafawa Balewa yayin da aka sanya wa katafaren sunansa. Remi Tinubu ta ziyarci jihar Kwara domin bude aiki.
Rahotanni sun bayyana cewa wata tankar mai da ke gudun wuce sa'a ta yi hatsari da wata mota da ke ajiye a gefen titi a jihar Neja lamarin da ya sa ta fashe nan take.
Gwamnatin Jigawa ta ware Naira biliyan 4.8 don ciyar da mabukata 189,000 a Ramadan. Haka kuma, za a gyara asibitoci 114, wanda zai ci Naira biliyan 9.7.
Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Mohammed ya naɗa sababbin masu ba shi shawara ta musamman, za a ba su rantsuwar kama aiki yau Talata, 28 ga Janairu, 2025.
Yayin da ake ta ce-ce-ku-ce kan raba awaki, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kare shirin yana cewa naman awaki na da amfani sosai wajen magance cututtuka.
Wasu 'yan daba sun lakada wa wata jami'ar Hukumar Tsaro ta NSCDC duka har ta fadi sumammiya a jihar Kwara yayin da ake bikin nadin sarauta a birnin Ilorin.
Tarwatsewar wani abun fahewa a Sabon Pegi, Mashegu, ya yi sanadiyyar mutuwar mutum hudu, raunata shida, da lalata gidaje 12. Yushau, wanda ake zargi, ya tsere.
Peter Obi ya ce shi bai kwallafa rai a kan lallai sai ya zama shugaban kasa ba amma yana bukatar Najeriya ta gyaru ta hanyar samar da shugabanci mai inganci.
Arewa
Samu kari