Arewa
Dan majalisar wakilai Abdussamad Dasuki ya gwangwaje yan mazabarsa da tallafin Naira miliyan 100 domin azumin Ramadan a jihar Sokoto da ke Arewacin Najeriya..
Dan uwan Malam Nuhu Ribadu ya zama sarki bayan Gwamna Ahmadu Fintiri ya nada shi a matsayin Sarkin Fufore, sabon masarautar da aka kafa a jihar Adamawa.
Da safiyar yau Talata 4 ga watan Janairun 2025 aka yi jana’izar marigayi, Alhaji Bala Albabello wanda shahararren ɗan kasuwa a Zaria da ke jihar Kaduna.
Hadimin Bola Tinubu a bangaren tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya bukaci Hajiya Naja’atu Muhammad ta janye kalamanta a wani bidiyon TikTok da ya ce na bata suna ne.
Shugaba Bola Tinubu ya rattaba hannu kan dokar kafa hukumar raya shiyyar Arewa ta Tsakiya (NCDC), kwalejin kimiyya a Rano, Kano da jami’ar kiwon lafiya a Tsafe.
Masu garkuwa sun kashe mutum ɗaya, sun sace huɗu a jihar Filato. Shugaban ƙaramar hukuma ya yi kira da a ceto su, ya kuma ziyarci yankin don tantance lamarin.
Kachallah Bammi Yarma ya dawo Katsina bayan shekaru tara a gidan yari a kasar Nijar. Bayyanarsa na iya ƙara tashin hankali a yankin Arewa maso Yamma.
An sake samun wani sabon bidiyo da ya nuna Kachallah Bugaje wanda ya koma Zakiru yana jagorantar addu’a tare da yaransa, bayan da ya ce ya daina ta’addanci.
Wani dan Arewa a shafin sada zumunta ya nuna goyon bayansa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu. Hakan ya sanya mutane da dama sun yi masa rubdugu.
Arewa
Samu kari