Arewa
Aƙalla mutane takwas ne suka samu raunuka bayan bindigar mafarauci ta tashi ba da gangan ba yayin taron cocin LCCN a karamar hukumar Demsa da ke jihar Adamawa.
Sanatoci daga Arewacin Najeriya sun ja hankalin gwamnatin tarayya da Bola Tinubu kan titunan Arewa. Sanata Goje da Sanata Sani Musa sun yi kira ga gwamnati.
Majalisar Dokokin Jihar Benue ta dakatar da mambobinta 13 da suka nesanta kansu daga tsige alkalin jihar, mai shari'a, Maurice Ikpambase a zamanta na ranar Talata.
Aliko Dangote ya samu sabon matsayin cikin jerin masu kudin duniya, Ya dawo na 86 daga na 144 a duniya. Dangote ya shiga cikin masu kudin duniya 100.
Majalisar dokokin Benue ta tsige Babban Alkalin Jihar, Maurice Ikpambese, bisa zargin take dokoki, cin hanci, da karkatar da kudaden shari’a bayan kuri’a.
Hatsabibin dan fashi a jihar Zamfara, Gwaska Dankarami, na shirin mika wuya bayan arangama da Sani Dangote inda wasu suka ce ana nemansa ruwa a jallo.
Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta fara bibiyar kungiyoyi masu zaman kansu dake jihar domin tabbatar da inda suke samun kudin gudanarwa bayan zargin da aka yi wa USAID.
Kungiyar 'Arewa Consultative Forum' ta ce samar da hukumomin raya shiyyoyin Arewa maso Gabas da Yamma za su tallafa wajen ceto yankin daga durkushewa.
Sanata Ali Ndume ya bayyana cewa bai dace Najeriya ta yi shiru a kan zargin dan majalisar Amurka da ke cewa kungiyar kasarsa ta USAID ta na da hannu a Boko Haram ba.
Arewa
Samu kari