Arewa
An yi ta yada bidiyo dauke da matasa 89 da aka ce sun je Lagos daga Katsina domin yin aiki a matatar Aliko Dangote, yan sanda sun yi bincike da tabbatar da gaskiya.
Bayan harin yan bindiga a Bauchi, Gwamna Bala Mohammed ya tabbatar da mutuwar ‘yan bindiga fiye da 60 a harin da ya faru a kauyen Mansur na karamar hukumar Alkaleri.
Jama'a da dama sun rasa muhallansu yayin da aka yi wata guguwa mai ƙarfi haɗe da ruwan sama a wasu sassan jihar Katsina, ciki har da wasu sababbin ma'aurata.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa.jihar ba ta samun ko sisin kwabo daga hakar ma'adanai. Ya fadi shirye-shiryen da yake don canza hakan.
Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya ce matakan da gwamnatinsa ta ɗauka tun da ya karɓi mulki sun taka rawa wajen inganta tsaro fiye da yadɗa ya tarar a jihar.
Mai martaba sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari ya gayyaci manyan malamai an yi taron addu'a ga shugaban ƙasa Tinubu, gwamnan Kwara da Najeriya.
Gwamna Dauda Lawal ya ce ya tarar da asusun gwamnatin Zamfara ba kudi, sai wata N4m. Amma ya ce yanzu ya biya basussukan albashi, NECO, WAEC da na wuta.
Bayan Sarkin Hausawa a Enugu ya karbi muƙami a gwamnati, matasan Arewa a jihar sun soki basaraken, Yusuf Sambo II, bisa amincewa da mukamin hadimin gwamna.
Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya kafa tarihi a fannin hakar ma'adanai a Najeriya. Gwamnan ya kafa masana'antar sarrafa lithium ta farko a kasar nan.
Arewa
Samu kari