Arewa
Cocin Katolika na Wukari a jihar Taraba ta tabbatar da rasuwar Fasto Nicholas Kyukyundu bayan doguwar rashin lafiya, yana da shekara 66 da haihuwa.
Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce tana binciken domin gano waɗanda ake zargi da hallaka wasu matan aure, uwargida da amarya, ta hanyar cinna musu wuta.
Mutum ɗaya ya mutu, shida sun ji rauni a turmutsutsin da aka samu a gidan Ministan Tsaro, Bello Matawalle a Gusau. An ce lamarin ya faru ne a ziyarar ministan.
Wata mata ta bayyana yadda wani mutumin Arewa ya dawo mata da wayarta ta iPhone da ta ɓata lokacin sauka daga keke a kasuwa cikin dabara da gaskiya.
Gwamnan jihar Katsina ya nuna alhini kan rasuwar Alhaji Nuhu Yashe, Bebejin Katsina, yana kiran wannan babban rashi ga iyalansa, al’umma da masarautar Kusada.
Gwamnatin jihar Bauchi ta bayyana cewa ta yanke shawarar kirkiro sababbin masarautu ne domin kusantar da harkokin mulki da ayyukan ci gaba ga al'umma.
Sanannen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi, ya musanta rade-radin da cewa ya tsere zuwa Turkey saboda barazanar Donald Trump.
Fadar shugaban kasa ta ce rikicin Arewa ta Tsakiya ya samo asali daga mallakar ƙasa, ta’addanci da satar ma’adinai, yayin da Tinubu ke ƙarfafa zaman lafiya.
Shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) a jihohi 19 na Arewa, Joseph John Hayab, ya warware zare da abawa kan barazanar da Donald Trump ya yi wa Najeriya.
Arewa
Samu kari