Abuja
Shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajuddeen, ya nada Alan Waka babban mataimaki. Masoya sun taya shi murna, suna addu’a Allah ya ba shi ikon sauke nauyi.
Karamin ministan tsaro a Najeriya, Bello Matawalle ya tsoma baki kan batun hana sojojin Najeriya 'visa' zuwa kasar Canada inda ya ce za su dauki matakin da ya dace.
Bayan korafe-korafen al'umma kan shirin 'Qur'anic Convention', rahotanni sun tabbatar da cewa an ɗage taron da aka shirya yi a Abuja cikin mako biyu.
Hon. Philip Agbese ya musanta hannu a zargin neman na goro daga jami'in kamfanin kudin crypto watau Binance, ya ba Tigran Gambaryan kwana 7 ya janye.
Bayan caccakar Canada da Nuhu Ribadu ya yi, ofishin jakadancinta a Najeriya ya mayar da martani kan rahotannin hana hafsan tsaron Najeriya shiga kasar.
Daya daga cikin sababbin limaman masallacin Abuja, Abdulkadir Salman Sholagberu ya bukaci yan Najeriya su koma ga Ubangiji kan tsadar rayuwa da ake ciki.
Yayin da ake ta korafi kan ƙirƙirar sababbin jihohi, Cibiyar Kare (CHRICED) ta zargi APC da amfani da lamarin don yaudarar 'yan Najeriya kan zaben 2027.
Tsohon shugaban inshora ta NHIS ya ce hukumar EFCC sun kama shi kamar sun kama Bello Turji. Ya fadi yadda ya zauna a wajen EFCC da zama a kurkukun Kuje.
Majalisar Wakilan Tarayya ta karrama marigayi tsohon shugaban mulkin soja a Najeriya, Janar Murtala Muhammed, ta ce za ta rika tunawa da shi a kowace shekara.
Abuja
Samu kari