Abuja
Gwamna Alia ya ce maharan da ke kashe mutane a Benue ba 'yan Najeriya ba ne, suna amfani da AK-47, suna magana da bakon yare, kuma suna da mafaka a Kamaru.
Hukumar kula da hannayen jari ta kasa (SEC) ta gargadi masu tallata shafukan bogi ko harkokin kasuwanci da ba su da rajista a kafafen sada zumunta a Najeriya.
Kamfanin mai na kasa watau NNPCL ya bi sahun matatar Ɗangote, an ga ya rage farashin kowace lita guda da man fetur a babbar birnin tarayya Abuja da Legas.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi kira ga Musulman Najeriya su zamo masu tausayi da adalci. Ya bayyana haka ne yayin wani taron kungiyar Ansa-ud-Deen a jihar Ogun.
Wasu yan Najeriya da dama sun yabawa Kamfanin NNPC bayan ya rage farashin litar man fetur zuwa N935 a wasu gidajen mai a Abuja, abin da ya faranta wa direbobi rai.
Fadar shugaban kasa ta ce ba wanda ya hana mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima shiga fadar Aso Villa. Ta ce labarin ba shi da asali bare tushe.
Sanata Barau I Jibrin ya bayyana cewa 'yan Najeriya sun aganin irin ayyukan alheri da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta ke aiwatarwa duk da matsaloli a duniya.
Shugaban APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya ce bai kamata birnin tarayya Abuja ya kasance a hannun 'yan adawa ba. Ganduje ya ce APC za ta kwace Abuja a 2027.
Jam'iyyar PDP a Abuja ta fara sayar da fom ga masu sha'awar tsayawa takara, inda ciyaman zai biya N8.5m, kansila N1.5m, mma mata za su samu fom din kyauta.
Abuja
Samu kari