Abuja
Shugaban manyan ma'aikatan Gwamnatin Tarayya, Tommy Okon ya bayyana cewa akalla ma'aikata dubu 5 za su samu matsala a albashin watan Disamba na wannan shekara.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana yadda ya tara N110bn cikin watanni uku da ya kwashe a kan kujerar ministan birnin tarayya Abuja.
Wasu matan aure a birnin tarayya Abuja sun fada hannun miyagun yan bindiga dauke da makamai bayan sun kai musu farmaki suna tsaka da gudanar da aikin gona.
Nyesom Wike ya fadi biliyoyin da ake bukata a karasa gidan mataimakin shugaban kasa. Bayan shekaru 13 da bada kwangilar, har yau ba a karasa gidan a Abuja ba.
Manyan hafsoshin tsaro da sufeto janar na ‘yan sanda (IGP), Kayode Egbetokun, sun bayyana gaban majalisar wakilan tarayyar Najeriya don tattaunawa kan matsalar tsaro
Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa 'yan Najeriya sun fi kowa wahalar mulka inda ya ce ya yi iya kokarin da zai yi, su ne alkalai.
Wani mai rajin kare hakkin dan Adam, Kwamred Emeke ya bukaci Shugaba Tinubu da ya kori Minista Wike daga mukaminsa kuma ya haramta masa rike mukami har abada.
Wasu miyagun ƴan bindiga sun kai farmaki a ƙauyen Yewuti na ƙaramar hukumar Kwali a birnin tarayya Abuja, inda suka sace mahaifin mataimakin shugaban ƙaramar hukuma.
Jami'an hukumar NDLEA, sun samu nasarar cafke wani hatsabibin dillalin kwayoyi, Ibrahim Momoh, da ke gudanar da ayyukansa a babban birnin tarayya Abuja
Abuja
Samu kari