Abuja
Shugaban gidan rediyon kare hakkin bil'adama da ke Abuja, Ahmed Isa ya dakatar da shirin Brekete Family saboda bacin rai kan gurfanar da kananan yaran Arewa a kotu.
Lauya mai kare yan zanga zanga ya yi kira ga malamai da yan siyasa kan yaran zanga zanga. Lauyan ya ce wulaƙanta yaran zanga zanga cin mutuncin Arewa ne.
Yayin da ake cece-kuce kan tsare yara ƙanana na tsawon watanni uku, Kungiyar Dattawan Arewa sun yi martani tare da yin Allah wadai kan matakin hukumomi.
Rahoton da muke samu ya bayyana yadda Farfesa Ibrahim Maqary ya ba da kudade domin a yiwa yaran da aka tsare a Abuja jinya kafin tabbatar da sun fito.
Wani lauya a Najeriya, Deji Adeyanju ya nuna damuwa kan rashin ganin sunayen wasu yara guda biyu a cikin waɗanda aka gurfanar a kotu a ranar Juma'a.
Ana zargin Nyesom Wike da yin rusau ba bisa ka'ida ba, inda ake zargin ya rushe gidaje sama da 100 nan take tare da jawo asarar kudin da suka yi kusan N200bn.
Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya shawarci 'yan Najeriya da su koma noma matukar suna son abubuwa su daidaita a kasuwa a daina ganin tsadar abinci.
Hukumar jarabawa ta JAMB ta tabbatar da cafke Farfesa kan yunkurin rubutawa yarsa jarabawa a 2019 inda aka yanke masa hukuncin daurin watanni shida.
Kungiyar SERAP ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gaggauta umartar a saki yaran da aka tsare da sauran masu zanga-zanga nan da sa'o'i 48.
Abuja
Samu kari